✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya

Hukumar ta bayyana cewa ta kai samame wajen ne tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro.

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta gano wani waje a Jihar Abiya da ake sake gyara da sabunta magungunan da suka lalace domin sayar wa jama’a.

A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook.

Hukumar ta ce an gano waɗannan magunguna a wasu gine-gine da ke garin Umumeje, a Ƙaramar Hukumar Osisioma Ngwa.

NAFDAC, ta ce wannan waje yana kusa da kasuwar Ariaria a Aba, cibiyar kasuwanci a jihar.

Hukumar ta bayyana cewa ta kai samame wajen ne tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro domin daƙile safarar jabun magunguna.

Wannan yana ɗaya daga cikin ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na kare lafiyar al’umma.