Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya ce, ya yi bakin cikin tuhumar da kotun da’ar ma’aikata CCT take yi wa alkalin alkalan Najeriya mai shari’a Walter Onnoghen akan laifin rashin bayyana kadarorinsa.
A ranar Litinin 14 ga Janairu 2019 ne, kotun ta yi zaman sauraran karar da aka shigar akan alkalin alkalan Najeriya.
Osinbajo ya bayyana wa kungiyar watsa labarai ta intanet (OPAN) hakan yau Laraba a Abuja, kuma yace shugaba Buhari bai da masaniya game da tuhumar da ake yi wa alkalin alkalan.