✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Na yafe wa Buhari —Ortom

Ni ma ina so Ubangiji Ya yafe min kurakuraina.

Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, ya ce ya yafe wa Shugaba Muhammadu Buhari duk wasu rashin daidai da ya aikata.

Ortom ya bayyana haka ne a yayin wata hira da ake yi da shi a shirin safiya na The Morning Show na tashar talabijin ta Arise a wannan Larabar.

Gwamnan ya kasance yana sukar fadar shugaban kasar a kan yadda ya ce Gwamnatin Tarayyar na sukar gwamnatinsa a kan kashe-kashen da ake yi a jiharsa.

A cewarsa, “Ya zama tilas na yafe wa Buhari, domin a matsayina na Kirista kuma kamar yadda ya tabbata a littafin addininmu, Ubangaji ba zai yafe maka ba idan ba ka yafe wa jama’a ba.”

A baya-bayan nan shugaban kasar ya nemi afuwa daga ’yan kasar da suke ganin mulkinsa ya kuntata musu.

Kazalika, Ortom ya kuma ya shawarci shugaban mai barin-gado da ya tsaya a kasar ya taimaka wa sabuwar gwamnati mai zuwa ta Bola Tinubu domin ciyar da kasar da ma jiharsa gaba, kamar yadda ya ce.