✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 15 sun mutu a sabon harin Kudancin Kaduna- ‘Yan sanda

Hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna sun tabbatar da rasuwar mutum 15 da raunata 24  yayin da wasu ‘yan bindiga suka kai wani sabon hari  a…

Hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna sun tabbatar da rasuwar mutum 15 da raunata 24  yayin da wasu ‘yan bindiga suka kai wani sabon hari  a garin Ungwan Pah II da ke unguwar Gwandara a  karamar hukumar Jama’a jihar Kaduna.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sandan jihar DSP Yakubu Sabo ya bayyana wa majiyarmu hakan.

Sabo ya ce, a yanzu haka Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ahmad Abdulrahman ya bayar da umarnin a binciko wadanda suke da alhakin kai harin a yankunan.