✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mun kashe ’yan ta’adda 52 a Borno da Yobe — DHQ

Dakaru sun samu nasarar ƙwato makamai da dama.

Hedikwatar Rundunar Tsaron Najeriya (DHQ) ta ce dakarunta sun yi nasarar kashe ’yan ta’adda 52 da kama 53 a wasu samame da suka kai jihohin Borno da Yobe.

Mai magana da yawun DHQ, Manjo-Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan yana mai cewa an kuma samu ’yan ta’adda bakwai da suka haɗa maza biyar da mata biyu da suka miƙa kansu ga sojojin.

Janar Buba ya ce an kuɓutar da mutum 61 da aka yi garkuwa da su a wurare daban-daban da ke ƙasar.

Ya kuma ce dakarun Operation Haɗin Kai a yankin Arewa maso Gabas, sun yi artabu da ’yan ta’addan a lokacin da suka kai samame, inda suka samu nasarar ƙwato makamai da dama.

A ɗayan ɓangare, ya ce dakarun Operation Delta Safe sun samu nasarar kama masu satar ɗanyen man fetur, inda suka kwace lita 496, 250 ta ɗanyen mai, injunan tuka-tuka guda huɗu, jiragen ruwa biyar da tankunan ajiye mai 57 da sauransu.

Janar Edward ya ce baya ga wannan, sojojin sun kwato harsasai daban-daban daga wajen masu aikata ta’asar.