✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

MU SHA DARIYA

Banufe da matarsa Wani Banufe ne Allah Ya jarabce shi da wata fitinannoyar mata. Ba ta raga masa wajen fitina. Shi ya sa kullum idan…

Banufe da matarsa

Wani Banufe ne Allah Ya jarabce shi da wata fitinannoyar mata. Ba ta raga masa wajen fitina. Shi ya sa kullum idan ya fita, sai ya bari sai ta yi barci sannan ya dawo gida. Wata rana sun yi fada da rana, ya fita daga gidan, sai Banufe ya dawo gida tsakiyar dare. Sai ya iske matar tasa a kwance tana sharbar barci. Ganin haka sai ya ce: “Allah na gode maKa, wannan fitinar ta yi barci.” Yana rufe baki sai nan take matar ta farka kuma ta maida masa martani da cewa: “Allah kuma Ya tsine wa wanda ya tashe ta ba!”

Daga Bashir Yahuza Malumfashi, 08065576011

 

Biyu babu

Wani Babarbare yana neman auren wata bazawara sai ta ce masa: “Ka aske gemunka kuma ka saki matarka, sannan mu yi aure.” Shi kuma sai ya aikata haka. Washegari ya je wurinta sai ta ce masa: “Ina gemunka?” Ya ce: “Ba kin ce in saki matata kuma in aske gemu ba?” Sai ta ce: “To, ashe kana jin maganar mata saboda haka ba zan aure ka ba, domin wata rana in ka ga wata in ta ce ka sake ni za ka aikata.”

Daga Malam Sajo Gombe, 08136709076

 

Rogo ko kyandir?

Wani Bakano ne mutumin kauye, aka kawo shi asibiti a birni, ba ya da  lafiya. Yana kwance a gadon asibiti sai aka dauke wutar lantarki, sai aka a bi daki-daki ana rarraba kyandir. Bakano da aka zo aka ba shi kyandir kawai sai ya kama ci. Aka zo gadonsa babu haske, aka tambaye inda ya aje kyandir da aka ba shi, sai ya ce: “Babu wanda ya ba ni fitila, rogo marar dadi kawai aka ba ni kuma na cinye.”

Daga Garba Sabiyola Gashuwa, 08096284154

 

Dan Najeriya

Wani dan Najeriya ne ya je kasar waje sai ’yan sanda suka biyo shi za su kama shi, sai ya shiga wani gidan rawa, suka rasa yadda za su yi. Sai wani Bature ya ce: “Ku kashe wutar lantarkin wurin.” Sai aka kashe, bayan minti uku ya ce a kunna. Ana kunnawa, abinka da dan Najeriya sai ya ce “Up NEPA!” Sai Baturen ya ce: “Ga shi can, ku kama shi.”

Daga Zayyanu Mai-Arsenal Tsafe, 08067051197