Wani matashi a Jihar Ebonyi mai suna Ekene Ezeogo ya tokari mahaifiyarsa mai suna Misis Mary Ezeugo wanda ya yi sanadin ajalinta tsohuwar mai shekara 60. Da haihuwa wannan lamari ya faru ne a layin Agbaja, da ke garin Abakaliki, babban birnin jihar.
Yadda lamarin ya faru kamar yadda Aminiya ta samu labari, Ezeogo yana fada ne da kanwarsa ita kuma mahaifiyar tasu ajali ya yi kiranta ta zo tana raba su lokacin kuma ya kawowa kanwar tokari ya naushe ta ta fadi kasa warwas a sume. kanen wanda ya yi kisan mai suna Onyema Ezeogo, ya ce yayansa tokarin uwar ya yi a ciki ta fadi kasa. Abin da ya yi sanadin mutuwar uwar su ke nan ko motsawa ba ta yi ba,” inda a cewarsa: “lokacin da ta zo raba su fada da yayansa shi kuma sai ya daga kafa ya shure ta ta fadi a kasa.”
Babban da ga marigayiyar, wanda likita ne a asibitin Agatha Lawrence Ezeogo, ya ce ko da aka garzayo da ita asibiti kafin ma a yi mata maganin gaugawa ta riga ta mutu sakamakon naushin kafa da Ekene ya yi mata.
Aminiya ta tuntubi mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar Jude Madu, inda ya ce: “Sun samu labari, kuma sun kama wanda ake zargi yana da hannun. Kuma da zarar sun gama bincike za su mika shi kotu in ya so ta yi nata aikin.”