✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu garkuwa da mahaifin tsohon Gwamnan Filato sun shiga hannu

Wannan ne karo na biyu da ake sace shi a kauyen na Mushere.

Mambobi shida daga cikin gungun wadanda suka yi garkuwa da mahaifin tsohon Gwamnan Jihar Filato, Joshua Chibi Dariye sun shiga hannu a Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, Ubah Gabriel wanda ya tabbatar da hakan a Jos ranar Lahadi, ya ce an sami nasarar kama su ne a wata maboyarsu bayan wani samame da jami’ansu suka kai.

An dai sace Chibi Dariye ne a watan Yunin 2020 a kauyen Mushere da ke Karamar Hukumar Bokkos da ke Jihar.

Tun lokacin dai ba a san inda yake ba sai a makon da ya wuce da aka gano tare da cafke masu garkuwa da shi.

Rahotanni na nuna cewa wannan ne karo na biyu da ake sace mahaifin tsohon Gwamnan a gidansa da ke kauyen na Mushere

Ko a shekarar 2015 ma sai da aka sace shi kafin daga bisani a sako shi bayan an biya masu garkuwa da shi kudin fansa.