Fadar shugaban kasar Najeriya ta mayar wa tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo martani a cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta bukace shi da ya je gaban kwararren likita domin duba lafiyarsa, sannan ta yi masa fatan samun lafiya.
Obasanjo ya ce, matsalar tsaro ta tabarbare domin kuwa ana ci gaba da garkuwa da mutane a sassa daban daban na kasar, baya ga kungiyar Boko Haram da ya ce, tafi samun karsashi a yanzu fiye da mulkin Shugabannin baya.