Majalisar dokokin jihar Osun ta umarci jami’an tsaron jihar sun kama duk wani mashayin taba sigari a cikin jama’a don tabbatar da dokar jihar na hana shan sigari.
Shugaban majalisar dokokin jihar Timothy Owoeye, ne ya sanar da hakan yau Alhamis a zauran majalisar da ke Osogbo babban birnin jihar.
An dai bayar da umarnin ne a daidai lokacin da kungiyar da ke yaki da yaduwar cututtuka suke gangamin bayyana illar yaduwar cututtuka a tsakanin jama’a a jihar.