Majalisar kasa ta Najeriya ta amince da tsayar da Naira dubu 27 a matsayin karamin albashin ma’aikata a jihohi. Yayin da Majalisar ta kuma amince da Naira dubu 30 a matsayin karamin albashi ga ma’aikatan gwamnatin tarayya.
A yau Talata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranci taron majalisar a fadarsa wadda ta kunshi tsofaffin shugabanni da tsofaffin alkalan alkalan Najeriya da kuma gwamnoni da shugabannin majalisa.
Ministan kwadago na Najeriya Chris Ngige ya bayyana cewa, za a mika kudirin ga majalisa a ranar Laraba domin amincewar ta.