✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Maina zai bayyana idan gwamnati ta bayar da tabbacin tsaron lafiyarsa

Iyalan Tsohon Shugaban Kwamitin Shugaban kasa na Gyaran Fansho, Abdulrasheed Maina sun ce tsohon shugaban kwamitin fanshon wanda aka kora daga aiki zai bayyana idan…

Iyalan Tsohon Shugaban Kwamitin Shugaban kasa na Gyaran Fansho, Abdulrasheed Maina sun ce tsohon shugaban kwamitin fanshon wanda aka kora daga aiki zai bayyana idan gwamnati ta basu tabbacin tsaron lafiyarsa.
Iyalan nasa sun bayyana haka ne a taron manema labarai da suka kira a Kaduna a ranar Laraba.
“Kamar yadda kuka sani a baya an yi ta kai wa Maina hari, saboda haka darasin da muka samu a baya ya koya mana darasi amma idan aka ba mu tabbacin tsaron lafiyarsa zai bayyana daga inda yake kuma ya gayawa ’yan Najeriya gaskiya”. Inji Mai Magana da Yawun Iyalansa, Aliyu Maina