✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Likitoci sun janye zanga-zangar da suka shirya

Likitoci Masu Neman Kwarewa sun janye zanga-zanar gama-garin da ta shirya farawa a fadin Najeriya a yau Laraba.

Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa (NARD) ta janye zanga-zanar gama-garin da ta shirya shiga a fadin Najeriya a yau Laraba.

Shugaban kungiyar, Dokta Orji Emeka Innocent, ya ce majalisar kolin kungiyar ta yanke shawarar ne bayan taron da ta yi ranar Laraba da dare.

Sai dai ya ce cikin sa’o’i 72 masu zuwa kungiyar za ta sake zama ta kara nazari kan matakin janye zanga-zanar.

Da farko NARD ta shirya gudanar da zanga-zanga a kullum ta hanyar rufe cibiyoyin lafiya mallakin gwamantin tarayya daga karfe 10 na ranar Laraba 9 ga watan Agustan nan da muke ciki.