✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Liberpool tana zawarcin dan kwallon Najeriya Ndidi

Dan kwallon kulob din Leicester City na Ingila kuma daya daga cikin ’yan kwallon Super Eagles ta Najeriya, Wilfred Ndidi watakila ya canza sheka zuwa…

Dan kwallon kulob din Leicester City na Ingila kuma daya daga cikin ’yan kwallon Super Eagles ta Najeriya, Wilfred Ndidi watakila ya canza sheka zuwa kulob din Liberpool na Ingila a karshen kakar wasa ta bana kamar yadda jaridar Mirror ta Ingila ta kalato a farkon makon nan.

Ndidi dan shekara 21, ana sa ran  zai maye gurbin dan kwallon tsakiya a kulob din Liberpool kuma haifaffen kasar Jamus Emre Can da ake ganin zai bar kulob din a karshen kakar wasa ta bana.

Ndidi wanda tauraruwarsa ke haskakawa a kulob din Leicester bayan da ya koma kulob din daga Genk a watan Janairu, 2017 yana cikin ’yan kwallon da za su yi wa Najeriya kwallo a yau Juma’a da kasar Poland a wasan sada zumunta.

Kawo yanzu ya buga wa Najeriya wasa sau 14 bayan da aka fara gayyatarsa a shekarar 2016 sannan ya buga wa kulob din Leicester City wasanni 30 kawo yanzu a kakar wasa ta bana.