✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Laulayin alayen lauye-lauye

Logar layancewar lulaye Limbu-limbun buzaye Luggar bebaye Lambun laujen lanjaye Laulayin alayen lauye-lauye   Laulayin lauye-lauye Laulawar lulaye Lambatun masu alaye Jimamamin jaye-jaye Mahukunta sun…

Logar layancewar lulaye

Limbu-limbun buzaye

Luggar bebaye

Lambun laujen lanjaye

Laulayin alayen lauye-lauye

 

Laulayin lauye-lauye

Laulawar lulaye

Lambatun masu alaye

Jimamamin jaye-jaye

Mahukunta sun yi maye

 

Fara’ar fuskokin furanni

Fatattakar fannoni

Farin dangon dausayi

Farmakin ga da tsautsayi

Fatanmu aiki da tunani

 

Sai an kawo sauyi

Ya ya za a yi

Mu hau bisa layi

Wasu ba su da tausayi

Garwashi ya zam gawayi

 

Sutura ta kamala

Ta haifar da takala

Tuntun kwarewa ta sagala

Lullubin ka ta makala

Kun ji sabuwar kutungwila

 

Na tsaya ina lalalala

Ko miyau zai malala

An hana lauya ta sakata ta wala

Ana ta yada juhala

An kauce wa adala

 

Matsiyata na bukatar bulala

’Yan wala-wala

Masu yada badala

Sai sun yi tsallen tsula

Tuni na cire musu hula

 

Ka ji kinbibi

Wai an hana daura kallabi

Ko sanya hijabi

Lamarin ba ya turbar adabi

dabi’un miyagu na da aibi

 

Kada a maishemu zabi

Masu bin labi-labi

Kan mai uwa da wabi

Kulorar ga akwai jangahur da zabibi

Dabarbarun ga ba sa cikin kitabi

 

Mun fasko masu haramta bobo

Da kwambo

Wai kada ai bokoko

Don kar mu sa mu na koko

Dabarar ga ba wani abu sabo

 

Mazan lauyoyi na da jallabiya

Matansu sanye da abaya

Tuntun ka tsororuwar kurya

Silin gashin makitsiya

A baza buya-buya

 

Kun ji aikin gaye-gaye

Kai duka ya kwaye

Buyagin baubawa ya zuganye

Masu ilimi kansu ya waye

Yau daliba tai muku tawaye

 

daliba ta samu kima

Da karin karama

Ai mata sallama

Ta samu salama

Kowa yai azama

 

An fasko masu karma-karma

Da ke ta tuma

Dundumin duman dama-dama

Masu jiji da kai da takama

Mugga masu halin kunama

 

Ana ta kai-kawo

Batutuwa babu awo

Dama-damar damun dawo

Juyin muciyar tukin tuwo

Wasan wutar kara wowo

 

Malam da malama

Mun gano masu takaddaama

Safe da yamma

Babu ko wata tantama

Mun ga kalma da kalama

 

Dukan dokoki

Bankar hayaki

Sai mai shan tabar buki

A runtumi auran shawaraki

Zabari ba burki

 

Kowa na da ’yanci

Ai tsaikon sasanci

A kiyayi rashin adalci

A daina duk wani batanci

Balle aikin ta’addanci

 

Ilimi ko ado

Tsarin rashin kangado

Rayuwar ramin kwado

Ko wasan kada ’ya’yan ludo

Tsunduma kogi ka tsunko bado

 

Mu bi doka

Kada kowa ya koka

Rani damina da kaka

A daina dan hankaka

A kiyayi warwarar tufka

 

karshen makon da ya arce na shiga birnin Dabo, inda ba a dabo, har ’yan dugwi-dugwi suka yi mini kabo da adabo, kodayake dai oyoyo Baba suka yi. Bayan da na kimtsa tsaf sai na fara bibiyar abin da aka tsuwurwurta a farfajiyar Balan-balan din sama, inda Fici da Bobo suka yi mini wake-wake, har ma da sauran nau’ukan watsattsake da buda wagagen littafai. Bayan mun kammala Bobo da kwambon bokoko sai na tuntubesu kan abin da suka koyo a Islamiyya nan da nan wata ’yar dugwi-dugwi da ke karatu kusa da gidan Maman Bebi can a tsaunin gwagware ta yi mini wani karatu, wai cewa:

A’ishatu fil Jami’a

A’isha ita ce mafificiya

Wannan likita ce

Waccan malama ce

 

Kai bari in kara:

 

Waccan lauya ce

Ana ta yi mata ce-ce-ku-ce

Ilimi da hijabi an yi kawance

Ni dai iyakata kwatance

Haurobiyawa sun iya zaurance

 

Hakika batun ’yar karama mai bobo da kwambon bokoko da sallama da salama a Islamiyya ya yi matukar burgeni, don haka ma na jadadda cewa lallai a biya direbobin alli da malaman Islamiyya ladar la’adar kwadago ko da da kadago ne, ba tare da la’akari da wulwulawar agogo ba.

’Yan makarantar Dodorido ba so nike in cika ku da surutu rututu ba, musamman jin cewa A’isha ita ce a jami’ar, kamar yadda karamar ’yar dugwi-dugwi ta rera mini, illa dai kawai ina son nusar da ku wani muhimmin lamari da ya dugunzuma ni cikin dundumin damuiwa, wato LAULAYIN LAULAWAR ALAYEN LAUYE-LAUYEN DOKOKI a kasar Haurobiya, musamman yadda na ji kafafen yada kwakwazo ana ta yamadidi da wata daliba Amosa Firdausi ’yar AbdusSalam da ta zo karbar shaidar kwarewarta aka hanata, wai saboda ta yi lullubin kai, sannnan ta dora tuntun kwarewar lauye-lauyen dokoki a sama.

Lamarin lauya mai kallabi ya kara tabbatar mini akwai miyagun boye da ke kokarin HARAMTA BOBO DA kWAMBON BOKOKO. Ni dai na fada na kara fada AI BOBO DA kWAMBO SAI dAN BOKO. Ina nan a garin TAKO-TAKO CIKIN dAKIN KATAKO ina lalube NA-KOKO in ga wanda zai zo ya haramta mini Bokokon!

Hakika an yi wa wannan lauya ta’addanci a daidai lokacin da ake ta fafutikar tabbatar da ’yanci babu ’yan cici. Baban-burin-huriyya da Usainin-Babajo kada ku bari a yi ta rawar banjo kan wannan lamarin, domin Baba-Ojo ya kammala digirin-digirgir a jam’in jama’ar jami’ar karatun dogon zango.

Haurobiyawa lokaci ya yi da za mu fifita sanya sutura ta kamala bisa tsarin al’adunmu, ba tare da mun cusguna wa wani ba. Idan kuwa an yi wa dokoki ’yan gyare-gyare irin na gyare da kurege, wajibi ne a nusar da mu, ta yadda za mu tsige ’ya’yanmu daga makarantun da ke tauye hakkokin al’umma a duk sa’adda suka kammala jami’a.

Ni dai nasan a daukacin fadin duniya Jam’in jama’ar jami’o’i ke yaye zakakuran direbobin alli, wadanda a kodayaushe suke horar da masu lauye-lauyen dokoki don tabbatar da ’yanci, ta yarda za a kauce wa shiga kunci. Haurobiyawa kada mu yi butulci, wannan aikin wawanci ne a karni na karamin lauje da sili. Ko so ake yi mu rika bobo da kwambo da walki ko mu tube zigidir, har da an hango mu a ce ahir ko ma wasu su ce tur?! To haihata-haihata atafau ba zan yarda da tafka ta’asa irin wannan ba, musamman a farfajiyar koyon watsattsake da buda wagagen littattafai da mujallu da makalu da jaridu da ke cikin Amintacciyar jaridar kasar nan.