✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kungiyar NLC ta yi kiran a kara albashi

Shugaban Kungiyar Ma’aikata reshen jihar Kwara, Mista Abdulyekeen Agunbiade ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta sake duba batun karin albashin ma’aikatan kasar nan. Shugaban…

Shugaban Kungiyar Ma’aikata reshen jihar Kwara, Mista Abdulyekeen Agunbiade ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta sake duba batun karin albashin ma’aikatan kasar nan.
Shugaban ma’aikatan ya yi kiran ne a garin Ilorin yayin da yake tattaunawa da manema labarai kan halin da kasar take ciki.
Ya kara da cewa kamar yadda dokar ma’aikata ta tanada za a rika duba albashin ma’aikata duk shekara 10.