✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotun Ƙoli: APC da NNPP sun ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya a Kano

Shugabannin NNPP da APC sun sanya hannu kan yarjejeniyar tabbatar da zaman lafiya a lokacin da bayan yanke hukuncin Kotun Ƙoli kan zaɓen gwamnan Kano

Jam’iyyun APC da NNPP a Kano sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a kan hukuncin da Kotun Ƙoli za ta yanke kan zaben gwamnan jihar.

Shugabannin jam’iyyun sun kulla yarjejeniyar ne a hedikwatar rundunar ’yan sandan jihar Kano a gaban kwamitin shugabannin hukumomin tsaro.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Usaini Muhammad Gumel, ya ce shugabannin jam’iyyun sun sabunta alkawarinsu na tabbatar da zaman lafiya a lokacin da kotu ta sanar da hukuncin da ta yanke da kuma a yayin bikin murnar nasara.

Ya ce taron ya tattauna kan wasu miyagun ’yan siyasa da ke yunkurin haɗawa tashin hankali a jihar, sannan ya yaba wa shugabannin APC da NNPP kan yadd tsayuwarsu a karo na bisa alkawarin da suka dauka da farko na zaman lafiya.

Usaini Gumel ya ce taron ya kuma tattauna kan matsalar shugabanci a cikin jam’iyyun biyu a wasu kananan hukumomin jihar.