✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto

Kotu ta soke zaben Gwamnan Bayelsa

Kotun ta ba da umarnin sake zabe nan kwana 90

Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Jihar Bayelsa da ke zama a Abuja ta soke zaben Gwamnan Jihar Bayelsa, Duoye Diri, da mataimakinsa, Lawrence Ewhrudjakpo.

Kotun mai alkalai uku a karkashin jagorancin Mai Shari’a Ibrahim Sirajo ta soke zaben ne bayan amincewa da korafin Jam’iyyar ANDP na cewa ba a sanya ta a zaben da aka yi a 16 ga Nuwamban bara ba.

Tuni kotun ta ba da umarni a sake zaben cikin kwanaki 90 masu zuwa.

%d bloggers like this: