✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kofin Afirka na mata: Afirka ta Kudu ta doke Najeriya

Afirka ta Kudun ta fanshe doke ta da Najeriya ta yi a wasan karshe na gasar ta karshe da aka buga a 2018.

Tawagar Banyana Banyana ta kasar Afirka ta Kudu ta doke takwararta ta Super Falcons ta Najeriya da ci biyu da daya.

A wasan wanda shi ne na farko a Gasar Cin Kofin ta Mata wato WAFCON, Afirka ta Kudun ta fanshe doke ta da Najeriya ta yi a wasan karshe na gasar ta karshe da aka buga a shekarar 2018.

Bayan zuwa hutun rabin lokaci babu ci, tawagar Banyana Banyana ta mamayi Super Falcons, inda ta zura mata kwallo biyu a jere a raga.

Jermaine Seoposenwe ce ta fara jefa kwallo a ragar Najeriya a minti 61 da fara wasa, sai minti 68 da fara wasa Hildah Tholakele Magaia ta kara kwallo na biyu.

Sai daga bisani ’yar wasan Najeriya da ke taka leda a kungiyar Atletico Madrid ta Spain, Rasheedat Ajibade ta farke kwallo daya a minti 91 da fara wasa.

Da wannan sakamakon, Najeriya za a iya cewa ta fara kafar hagu a shirinta na kare kambunta na gasar, da kuma kokarinta na lashe gasar karon na goma.

An buga wasan ne a Filin Wasa na Rabat, Babban Birnin Kasar Morocco.