✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kasashen da suka rage a Gasar Kofin Duniya ta ’yan kasa da shekaru 20

Koriya ta Kudu ta fatattako tawagar Flying Eagles ta Najeriya.

Yanzu haka ana ci gaba da fafatawa a Gasar Kofin Duniya ta ’yan kasa da shekara 20 wadda kasar Argentina ta kasance mai masaukin baki.

Koriya ta Kudu da Uruguay sun kai zagayen kusa da na karshe a gasar wadda Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya FIFA ke jagoranta.

Uruguay ta doke Amurka da ci 2-0 a Santiago del Estero, inda suka mamaye wasan daga farko har karshe kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ruwaito.

Ita kuwa Koriya Ta Kudu ta doke Najeriya ne da ci 1-0 bayan da aka kara lokaci.

Yanzu Uruguay za ta fafata da Isra’ila a ranar Alhamis yayin da Koriya ta Kudu kuma za ta gwada kwanjinta da Italiya don neman gurbi a wasan karshe.

Gasar ta bana wadda aka soma tun a ranar 20 ga watan Mayun da ya gabata ita ce karo na 23 da Hukumar FIFA ta shirya a tarihi.