✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kano za ta shirya gasar wasanni tsakanin kananan makarantun sakandare

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta shirya tsaf don fara gudanar da gasar wasannin kwallon kafa da na hannu da wasannin motsa jiki a…

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ta shirya tsaf don fara gudanar da gasar wasannin kwallon kafa da na hannu da wasannin motsa jiki a tsakanin kananan makarantun sakandaren da ke jihar.

Shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano Alhaji Ibrahim Galadima ne ya bayyana haka  a wajen taron da aka gudanar wanda ya kunshi kodineotocin wasanni na Ma’aikatar ilimi  na shiyya-shiyya da shugabbannin da sakatarori na kungiyoyin wasanni da kuma masu horar da ’yan wasa.

Alhaji Galadima ya bayyana cewa manufar gasar ita ce don a karfafa wa yaran gwiwa wajen bunkasa  fasaharsu  a fagen wasanni tun daga matakin farko wanda zai ba su damar waklitar jihar a matakin kasa a nan gaba.

Sai dai Shugaban  Hukumar wasannin ya bayyana rashin jin dadinsa game da rashin halartar da yawa daga cikin kodinotocin wasanni wajen taron inda ya bayar da tabbacin daukar matakin da ya kamata don ganin an magance wannan mummunar dabi’a.

Da yake bayani game da dokokin gasar Shugaban  Kwamitin Shirya gasar Farfesa Rabi’u Muhammad Chanhu ya bayyana cewa dalibai maza ne kadai za su buga wasannin kwallon kafa yayin da maza da mata za su taka rawa a sauran wasannin.