✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kada wanda ya kafa allunan taya ni murnar zama Minista – Wike

Ya ce aikin gina birnin ne yanzu a gabansa

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya hana karkafa duk wasu allunan talla da nufin taya shi murnar zama Minista.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na ma’aikatar, Anthony Ogunleye, Wike ya ce ya yanke shawarar daukar matakin ne saboda nuna kishin kasa da kuma mayar da hankali wajen aikin da Tinubu ya sa shi.

Sanarwar ta ce Ministan ya gode da fatan alherin, amma ya bukaci a dakatar da amfani da irin wadannan allunan tallan.

Wike ya ce babban burinsa shi ne ya bunkasa Abuja ta yadda mazauna cikinta za su ji dadin zamanta a zamanin mulkinsa.

Ya kuma ce ya yana matukar girmamawa da kuma mutunta bukatun mazauna birnin tare da jajircewa wajen ganin ya biya musu su.