✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kabiru Gaya ya fadi zabe bayan shekara 16 a Majalisa

Kawu Sumaila na Jam'iyyar NNPP ya lashe 10 daga cikin kananan hukumomi 16 da ke Kano ta Kudu

Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, da ke neman tazarce bayan shekara 16 a Majalisar Dattawa, ya sha kaye a hannun dan Majalisar Wakilai, Kawu Sumaila.

Kawu Sumaila na Jam’iyyar NNPP ya yi nasara ne bayan ya samu nasara a 10 daga cikin kananan hukumomi 16 da ke Kano ta Kudu.

Kawu Sumaila ya zama gwarzo ne bayan ya samu kuri’u 18,419 a yayin da Sanata Kabiru Gaya na Jam’iyyar APC kuma ya samu kuri’u 10,079.

Wanda ya zo na uku, dan takarar Jam’iyyar PDP, ya samu kuri’a 747.

A shekarar 2007 Kabiru Gaya, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya fara zama Sanata, kuma tun daga lokacin yake Majalisar Dattawa.