✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jerin ma’aikatun da Tinubu ya raba wa Ministocinsa

Ministoci 45 ne dai Tinubu ya raba wa ma'ikatun

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya fitar da jerin ma’aikatun da sabbin Ministoci 45 da ya nada za su yi aiki.

Sai dai sabanin yadda aka saba gani a bayan, Shugaban ya yi wa ma’aikatu da dama kwaskwarima, sannan ya raba wasu, wasu kuma aka canza musu fasali.

Kazalika, Aminiya ta lura cewa duk da cewa Jihar Kano ta rabauta da kujerun Ministoci guda biyu, dukkansu za su yi aiki ne a matsayin kaanan Ministoci.

Ga cikakken jerin ma’aikatun da kowanne Minista zai yi aiki:

Tahir Mamman – Ilimi

Yusuf Sununu – Karamin Ministan Ilimi

Mohammed Badaru – Tsaro

Bello Matawalle – Karamin Ministan Tsaro

Ahmed Dangiwa – Gidaje da Raya Birane

Abdullahi T. Gwarzo – Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane

Simon Lalong – Kwadago da Ayyuka

Hannatu Musawa – Al’adu

Atiku Bagudu – Kasafi da Tsara Tattalin Arziki

Mariya Mahmud – Karamar Ministar Abuja

Bello Goronyo – Karamin Ministan Ruwa

Abubakar Kyari – Noma da samar da Abinci

Yusuf M. Tuggar – Harkokin Waje

Sa’idu A. Alkali – Harkokin Cikin Gida

Ali Pate – Lafiya

Ibrahim Geidam – Harkokin ‘Yan Sanda

Maigari Ahmadu – Karamin Ministan Karafa

Shu’aibu Abubakar Audu – Karamin Ministan Karafa

Mohammed Idris – Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a

Nyesom Wike – Abuja

Lateef Fagbemi – Shari’a/Babban Lauyan Gwamnati

Imaan Suleiman Ibrahim – Karamar Ministar ‘Yan Sanda

Zephaniah Jisalo – Ayyuka na Musamman

Joseph Utsev – Ruwa da Tsafta

Aliyu Sabi Abdullahi – Karamin Ministan Gona da Samar da Abinci

Bosun Tuani – Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani

Ishak Salaco – Karamin Ministan Muhalli

Wale Edun – Kudi da Tattalin Arziki

Bunmi Tunji – Sufurin Jiragen Ruwa

Adedayo Adelabu – Lantarki

Tunji Alausa – Karamin Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a

Dele Alake – Ma’adinai

Lola Ade-John- Yawon Bude Ido

Adegboyega Oyetola – Sufuri

Doris Anite – Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari

Uche Nnaji – Kimiyya da Fasaha

Nkiruka Onyejeocha – Karamar Ministar Kwadago da Samar da Ayyukan Yi.

Uju Kennedy – Ministar Mata

David Umahi – Ayyuka

Festus Keyamo – Sufurin Jiragen Sama

Abubakar Momoh – Matasa

Betta Edu – Walwala da Yaki da Talauci

Ekperikpe Ekpo – Karamin Ministan Iskar Gas

Heineken Lokpobiri – Karamin Ministan Man Fetur

John Enoh – Wasanni

Majiyoyi daga Fadar Shugaban Kasa dai sun ce ba a kai ga sanya ranar rantsar da sababbin Ministocin ba, amma kwanan nan ake sa ran fara yi musu bita.