✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Isra’ila ta sa a cire tutocin Falasdinu daga gine-ginen gwamnati

Isra'ila ta ce tutar barazana ce a gareta

Ministan Tsaron Isra’ila Itamar Ben-Gvi, ya umarci ’yan sandan kasar da su cire tutocin Falasdinu daga dukkan gine-ginen gwamnati, inda ta bayyana tutar a matsayin ta “ta’addanci”.

Isra’ila dai kai tsaye ba ta haramta sanya tutocin Falasdinu ba, amma ’yan sanda da sojoji na da ikon cire su a duk lokacin da suka ga za ta kasance barazana gare su.

Umarnin Ministan na zuwa ne ranar Lahadi, kodayake ba sabon abu ba ne, amma Falasdinawa na kallonsa a matsayin wani yunkuri na murkushe su da karfin tuwo.

Kazalika, ba da umarnin ya biyo wata zazzafar zanga-zangar kin jinin Isra’ila da aka yi a birnin Tel Aviv ranar Asabar, inda wasu daga cikin wadanda suka yi suka rika daga tutocin Falasdinun.

Masu zanga-zangar dai sun rika yi Allah-wadai da gwamnatin Fira Minista Benjamen Netanyahu, inda suka rika neman a rika yin daidaito tsakanin Yahudawa da Falasdinu.

Adadin Falasdinawan da suke zaune a Isra’ila dai sun kai kusan daya bisa biyar na yawan jama’ar kasar, kuma galibinsu tsatson Falasdinawan da suka ki barin kasar bayan an kirkire ta a 1948.