Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA) ta bayar da tallafin kayayyaki na miliyoyin Naira ga ’yan gudun hijirar Boko Haram da wadanda ambaliya ko gobara suka shafa a sassan jihar.
Babban Sakataren Hukumar Dokta Aminu Gambo Waziri ya shaida wa Aminiya haka ta bakin Kakakin Hukumar, Malam Umar Muhammad haka a Katsina, inda ya ce, kayayyakin tallafin da hukumar ta bayar kuma take ci gaba da bayarwa sun hdda da abinci da tufafi da kayan gini da na kwanciya da kuma kudi.
Babban Sakataren ya ce a daminar bana hukumar ta kai agajin gaggawa ga kananan hukumomin da suka samu ambaliyar ruwa da suka hada Malunfashi da Dallaje a yankin Bindawa da Kankiya, Inwalar Jangehe da ke batagarawa, sai Kukasheka da ke kankara da kuma garin Kaita. Ya ce hukumar ta kai tallafi ga wadanda gobara ta shafa a garuruwan Faskari da Malunfashi da ’yan kasuwar Dankama da ke yankin Kaita da garin Mahuta da ke dandume.
Babban Sakataren ya ce, wadanda rikicin barayin shanu ya rutsa da su musamman na garin Dungun-Mu’azu da ke karamar Hukumar Sabuwa sun samu tallafin kudi daga hukumar.
Da ya juya ga ’yan gudun hijirar Boko Haram, Dokta Aminu ya ce, hukumarsa ta kai tallafi a sansanin ’yan gudun hijirar da ke Katsina da Dutsinma da Ingawa da Daura da Mai’aduwa da baure da Sandamu da Mahuta da kuma kafur, wadanda suka samu tallafin kayan abinci da tufafi da na kwanciya.
Ya ce nan gaba hukumar za ta kai tallafi a kananan hukumomin Kankiya da Kaita da Ingawa da Rimi da Bindawa da Kusada da Matazu da Batsari da kuma Katsina. Sai dai bai bayyana adadin kudin da hukumar ta fitar ba saboda kamar yadda ya ce, a lokacin da Aminiya ta ziyarci ofishin suna cikin shirin fita ne domin kai wasu kayan agaji a wasu wuraren.
Dokta Aminu ya ce, gwamnatin jihar a karkashin Gwamna Aminu Masari ne take samar da kayayyakin agaji, inda ya ce sau daya Hukumar Agajin Gaggawa ta kasa (NEMA) ta kai tallafi jihar.