Shahararren mawakin duniya dan asalin kasar Senegal da ke zaune a Amurka Akon, ya ziyarci Zawiyyar Fitaccen Shehun Malamin Islama Shaikh Ibrahim Nyass Kaulaha, da ke kasar Sanegal.
A ‘yan kwanakin nan tauraron na wakokin R&B wanda sunansa na asali Alioune Badara Thiam ya kudiri aniyar gina katafaren birni a kasar Sanegal domin farfadowa da bunkasa al’adun Afirka a tsakanin ‘yan Nahiyar mazauna Turai; Aikin da yac e zai lakume Dalar Amurka biliyan shida.
Kungiyar matasan Darikar Tijjaniya ta Fityanul Islam ce ta sanya hoton ziyarar da Mawaki Akon ya kai Zawiyyar a shafin ta na sada zumunta:
![](https://i0.wp.com/hausa.dailytrust.com.ng/wp-content/uploads/2020/09/FB_IMG_1599204801728-e1599214999771-536x400.jpg?resize=536%2C400&ssl=1)
![](https://i0.wp.com/hausa.dailytrust.com.ng/wp-content/uploads/2020/09/FB_IMG_1599204814803-e1599215102392-404x400.jpg?resize=404%2C400&ssl=1)
![](https://i0.wp.com/hausa.dailytrust.com.ng/wp-content/uploads/2020/09/FB_IMG_1599204817956-e1599215227196-436x400.jpg?resize=436%2C400&ssl=1)
![](https://i0.wp.com/hausa.dailytrust.com.ng/wp-content/uploads/2020/09/FB_IMG_1599204807022-600x338.jpg?resize=580%2C327&ssl=1)