✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hisbah ta lalata barasar N60m a Katsina

Hukumar ta buƙaci masu ruwa da tsaki a jihar su dage wajen sanya ido kan tarbiyyar matasa.

Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, ta lalata barasa da sauran muggan ƙwayoyi da ta ƙwace da kuɗinsu ya kai Naira miliyan 60 a Ƙaramar Hukumar Funtua.

Kwamandan Hisbah na jihar, Dokta Aminu Usman ne, ya sanar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a Katsina.

Ya ce sun ƙwace tare da lalata kwalayen giya 1,750 da jarkoki 33 na giya da aka sarrafa su a gida a Funtua.

Usman, ya bayyana cewa wannan aiki na daga cikin ayyukansu na inganta tarbiyy a jihar.

Ya jinjina wa ma’aikatan hukumar kan ƙoƙarinsu, inda kuma ya buƙace su da su ƙara azama wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Ya kuma roƙi shugabannin Addini a jihar da su tallafa wa hukumar, inda ya ce Hisbah ta kowa ce ba ta wani rukuni ba.

Usman, ya gode wa Gwamna Dikko Radda kan goyon bayan da yake bai wa hukumar.

Kazalika, ya buƙaci jama’a da su taimaka ta hanyar bayar da bayanai kan inda ake aikata ɗabi’u marasa kyau, sannan ya buƙaci iyaye, malamai, da shugabannin al’umma da su ƙara ƙaimi wajen koyar da matasa kyawawan halaye.