✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin Tudun Biri: Sojoji Sun Yi Ganganci —Hedikwakar tsaro

An samu wasu sojoji da hannu dumu-dumu a harin kuma za su fusknaci hukunci

Binciken Rundunar Sojin Najeriya kan harin “kuskuren” da jirgin soja ya kashe kusan mutane 100 a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna, ya nuna akwai ganganci a cikin harin.

Bayan daukar dogon lokaci tana bincike kan harin rundunar sojin ta ce, jami’an da suka yi wannan aika-aika za su fiskanci hukunci.

Ta ce ta samu wasu jami’an rundunar biyu da hannu dumu-dumu wurin faruwar lamarin, kuma tabbas za su fuskanci kotun soji, domin binciken su ya tabbatar da cewa tun farko bai kamata a saki bama-baman da aka jefa ba.

Daraktan yada labarai na hedikwatar tsaro ta Najeriya, Edward Buba, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya gudana a Abuja ranar Alhamis.

Tun da farko dai rundunar ta dauki alhakin harin, sai dai a wancan lokacin ta danganta lamarin da “kuskure.”

Da yake da karin haske, Edward Buba, ya ce an mika rahoton binciken ga wadanda suka dace, amma ba zai iya bude komai a kan lamarin ba har sai an gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotun soji.