✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Harin ta’adanci: Gwamnati ta nemi mutane kada su firgita

Gwamnatin Tarayya ta nemi mutane da kada su yi wata fargaba duk da gargadin da wasu kasashen yamma suka yi wa mutanensu masu shigowa Najeriya…

Gwamnatin Tarayya ta nemi mutane da kada su yi wata fargaba duk da gargadin da wasu kasashen yamma suka yi wa mutanensu masu shigowa Najeriya kan yiwuwar kai hare-haren ta’adanci.
Ministan Yada Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed shi ne ya yi furucin a sanarwa da ya sanya wa hannu a jiya inda ya bayar da tabbacin daukar matakan da suka dace don kare lafiya da dukiyoyin ’yan Najeriya da baki.