✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hamas ta karɓi tayin tsagaita wuta a Gaza

Har yanzu Firaminista Benjamin Netanyahu ya dage cewa yana son kawo ƙashen Hamas.

Ƙungiyar Hamas ta sanar da karɓar tayin tsagaita wuta a yaƙin Gaza kuma tuni ta soma nazarin sabuwar yarjejeniyar da aka gabatar mata.

Hamas wadda ta nuna alamun samun masalaha ta bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce kawo ƙarshen hare-hare Isra’ila da janye dakarunta daga yankin.

Ƙungiyar ta ce tana tuntuɓar abokan shawararta, sannan ta jinjina wa ƙoƙarin masu shiga tsakanin.

Shugaban Amurka ne ya gabatar da yarjejeniyar tsagaita wutar ta kwana 60, wadda ya ce tuni gwamnatin Isra’ila ta amince da ita.

To sai dai rahotonni na cewa da dama cikin ministoci masu ra’ayin riƙau ba su gamsu da ita ba, yayin da Firaminista Benjamin Netanyahu ya dage cewa yana son kawo ƙashen Hamas.