✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Filato ta sake dawo da dokar hana fita

Saboda haka Gwamnatin jihar a yanzu ta sake dawo da dokar hana fitar ta sa'o'i 24.

Wasu matasa sun fasa runbunan da aka ajiye kayayyakin abinci na tallafin COVID-19 da gwamnatin tarayya ta aikowa jihar Filato, don rabawa al’ummar jihar, suka wawushe kayayyakin a yau Asabar din nan.

Sakamakon haka ya sanya Gwamnatin jihar Filato ta sake dawo da dokar hana fita ta sa’o’i 24 da ta kafa, a ranar Talatar da ta gabata, bayan da ta sassauta dokar daga karfe 6 na safe zuwa 8 na dare, a jiya juma’a.

Wata sanarwa da gwamnan jihar Simon Lalong ya fitar ce ta bayyana haka.

Sanarwar ta ci gaba da cewa “an shimfida dokar takaita zirga-zirgar ne ganin abinda wasu bata gari suka yi a yau Asabar, na fasa rumbunan da aka ajiye kayayyakin abinci na tallafin annobar Covid-19 da gwamnatin tarayya ta aikowa jihar, da kuma ganin yadda wannan mummunan lamari yake neman ya ci gaba, ta yadda zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar.”

“Saboda haka Gwamnatin jihar ta sake dawo da dokar hana fitar ta sa’o’i 24, a kananan hukumomin Jos ta Arewa da Jos ta Kudu.”

“Gwamnatin jihar ta yi hakan ne domin tabbatar da tsaro da kare dukiyoyin al’umma wanda yanzu suke cikin barazana.”