✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Bauchi ta nada sabon Sarkin Jama’are

Alhaji Nuhu Ahmad Wabi ya maye gurbin mahaifinsa da ya rasu a farkon watan Fabrairu.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta nada Alhaji Nuhu Ahmed Wabi a matsayin sabon Sarkin Jama’are.

Sabon sarkin ya maye gurbin mahaifinsa, Alhaji Ahmad Mohammed Wabi, wanda ya rasu a farkon watan Fabrairu.

Sanarwa nadin sabon sarkin na dauke ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Ibrahim Alkassim Mohammed, ya fitar a ranar Litinin.

Alhaji Nuhu Ahmad Wabi ya kasance sarki na 10 da ya dare bisa karagar mulkin Masarautar Jama’are.

Kafin nadin nasa a matsayin sabon sarkin, shi ke rike da sarautar Yariman Jama’are.

Tuni al’ummar Jama’are suka shiga shewa da murna, bayan fitar sanarwar nadin sabon sarkin.