✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnati ta sanar da ranakun hutun kirsimeti, sabuwar shekara

Gwamnatin tarayya ta bayyana ranakun 25 Talata da 26 Laraba ga watan Disamba a matsayin ranakun hutun bukukuwan Kirismeti. Gwamnatin kuma ta bayyana ranar Talata…

Gwamnatin tarayya ta bayyana ranakun 25 Talata da 26 Laraba ga watan Disamba a matsayin ranakun hutun bukukuwan Kirismeti.

Gwamnatin kuma ta bayyana ranar Talata 1 ga watan Janairu na shekarar 2019 a matsayin ranar hutun sabuwar shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Abdurrahman Bello Danbazau ne ya sanar da hakan a madadin gwamnatin tarayya.