Shugaban kungiyar kwadago NLC ta Najeriya Ayuba Wabba ya ce, gwamnatin tarayya kwanan zata sanar da sabon albashi mafi karanci ga ma’aikatan kasar.
Shugaban ya bayyana hakan ne, bayan kammala ganawar kwamitin wanda zasu mika shi ga shugaban Najeriya Muhammadu Buhari don samun amincewarsa.
Wabba ya sanar da hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a Abuja.