✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnan Ondo ya mika wa Mataimakinsa mulkin Jihar, ya tafi neman lafiya

An yi ta guna-guni a 'yan kwanakin nan kan lafiyar Gwamnan

Gwamnan Jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, ya mika ragamar mulkin jihar ga mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa, inda ya tafi kasar waje hutun neman lafiya na kwana 21.

A cikin wata wasika da ya aike wa da Majalisar Dokokin Jihar ranar Talata, Gwamnan ya ce Mataimakin nasa zai rike kujerar a matsayin mukaddashi har lokacin da zai dawo.

Kakakin Majalisar, Oladimeji Oladiji, wanda ya karbi kwafin wasikar ya ce hutun Gwamnan zai kare ne ranar 6 ga watan Yulin 2023.

A cewar Kakakin, “Hutun, wanda ya fara ranar 7 ga watan Yuni, za a ci gaba da shi har zuwa ranar 6 ga watan Yulin 2023, saboda ranakun hutun da za a samu na Ranar Dimokuradiyya da kuma na Sallah Babba.

“Mataimakin Gwamna, Hon. Lucky Orimisan Aiyedatiwa ne zai rike masa ragama har zuwa lokacin da zai dawo ranar 6 ga watan Yulin 2023,” in ji wasikar.

A baya-bayan nan dai Gwamnan ya sha fama da rashin lafiya inda ba a cika ganinsa a wuraren taruka da ayyukan gwamnati ba a kai a kai.

Mutane dai sun yi ta korafi a kan haka, kodayake hadimansa sun sha musantawa, inda suka ce lafiyarsa kalau. Amma daga baya sun amince cewa yana fama da rashin lafiya.