✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu

An ƙaddamar da kwamitin ne a wani mataki na magance buƙatu daga al’ummomi daban-daban da kuma inganta al’adu da tsarin mulki na asali a faɗin…

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya ƙaddamar da wani babban kwamitin ƙirƙiro masarautu da gundumomin hakimai a jihar.

An ƙaddamar da kwamitin ne a wani mataki na magance buƙatu da dama daga al’ummomi daban-daban da kuma inganta al’adu da tsarin mulki na asali a faɗin Jihar Bauchi.

Gwamna Bala ya shaida wa kwamitin da ya sake duba buƙatu na samar da sabbin masarautu a faɗin jihar.

Ya ce, aikin kwamitin shi ne inganta harkokin gudanar da mulki na cikin gida da inganta al’adu da kuma ƙarfafa muhimmiyar rawar da sarakuna ke gudanarwa wajen haɗin kai da ci gaba.

Gwamnan ya bayyana matakin a matsayin alƙawarin da gwamnatinsa ta yi na tabbatar da adalci da haɗa kai da kuma ƙarfafa tsarin mulki da ci gaba a Jiha da ƙananan hukumomi.

Ya bayyanawa kwamitin da ya ba da shawarar al’ummomin da suka cancanta na sabbin masarautu, da ba da shawarar tsarin gudanarwa don ingantaccen aiki na sabbin masarautu, masarautu ko gundumomi da gabatar da cikakken rahoto tare da shawarwari masu dacewa cikin makonni takwas.

Gwamnan ya buƙaci kwamitin da ya gudanar da aikinsa cikin gaskiya da himma da kuma adalci.

Ya bayyana cewa, shirin na cika alƙawuran siyasa ne da nufin karkatar da hukumomi don samar da ingantattun ayyuka da kuma ƙara rarraba albarkatu.