Gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai ya sake lashe zaben Gwamnan jihar a karo na biyu kamar yadda hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta sanar.
Jami’in hukumar zaben jihar Farfesa Muhammed Yahuza Bello ya sanar da cewa, Gwamnan Kaduna kuma dan takarar Gwamnan jihar a jam’iyyar APC ya lashe zaben gwamnan jihar da kuri’u 1,045,427 yayin da abokin takararsa na jam’iyyar PDP Alhaji Isah Ashiru ya samu kuri’u 814,168.