A gobe Asabar idan Allah Ya kai mu za a fara Gasar Cin Kofin Duniya na Matasa ’Yan Kasa da shekara 17 a Brazil. Gasar wacce ke gudana duk bayan shekara biyu, a bana za a yi ta ce a kasar Brazil.
Ana sa ran kasashe 24 daga kowane bangare na duniya ne za su fafata inda za a dauki tsawon mako uku ana yi.
Kasashe hudu ne za su wakilci Nahiyar Afirka a wannan gasa da suka hada da Najeriya da Angola da Senegal da kuma Kamaru.
Najeriya ce ta fi yawan lashe wannan kofi a tarihi inda ta dauka har sau biyar. Ta fara dauka ne a 1985 sai a 1993 sai a 2007 sai a 2013 sai kuma a 2015.
Sai Brazil ke biye da ita inda ta dauka sau 3 sai kasashen Ghana da Meziko da suka taba dauka sau bibbiyu.
Najeriya da Ghana ne suka taba lashe wannan kofi daga Nahiyar Afirka a tarihin gasar.
Najeriya za ta fafata a Rukunin B da kasashen Hungary da Ecuador da Austireliya inda kasashe biyu da ke saman tebur a kowane rukuni za su haye matakin zagaye na biyu.
An fara gasar ce tun a 1985 kuma ake ci gaba da gudanar da ita duk bayan shekara biyu a kasashe daban-daban inda a wannan karo Brazil za ta karbi bakunci.
Masoya kwallon kafa a sassan duniya sun zuba ido su ga yadda gasar za ta gudana ciki har da na kungiyar Golden Eaglets ta Najeriya.
Fatarmu Allah Ya ba Najeriya sa’a ta lashe kofin a karo na 6.