✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobara ta yi ajalin wani mutum yayin da yake barci a gidansa

An ajiye gawar mutumin a ɗakin ajiye gawa na asibitin Yaba.

Wani mutum mai suna Obinna ya rasu lokacin da yake barci, bayan da gobara ta tashi a gidansa da ke yankin Iyana-Ipaja a Jihar Legas.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Benjamin Hundeyin ne, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) faruwar lamarin a ranar Lahadi.

Ya ce gobarar ta faru ne a ranar Asabar da misalin ƙarfe 7:30 na dare.

Hundeyin ya bayyana cewa ’yan sanda sun samu kiran gaggawa daga wani mutum game da gobarar.

“Babban jami’in ’yan sanda na yankin ya gaggauta zuwa wajen bayan samun kiran.

“Haka kuma, an sanar da hukumar kashe gobara game da lamarin. Amma, da aka kashe gobarar, an gano wani mutu ya mutu a sanadin gobarar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an ɗauke gawar mamacin zuwa ɗakin ajiye gawa na asibitin Yaba, kafin sanin musababbin tashin gobarar.

Ya ce ’yan sanda na gudanar bincike kan lamarin.