✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gobara ta hallaka mutane ta kone sama da gidaje 50 a Legas

Da safiyar ranar Lahadi ne al’ummar unguwar Abule Ado da ke yankin Festak a karamar hukumar Amuwo Odofin a jihar Legas, suka wayi gari da…

Da safiyar ranar Lahadi ne al’ummar unguwar Abule Ado da ke yankin Festak a karamar hukumar Amuwo Odofin a jihar Legas, suka wayi gari da karar fashewar wasu abubuwa wadanda suka yi sanadiyyar tashin gobarar da tayi salwantar rayuka da dama da kuma kone tare da lalata akalla gidaje 50 a yankin.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa, gobarar ta samo asali ne bayan da wata motar tifa da ke sauke kasa a yankin ta kama da wuta, inda nan take wutar ta yadu zuwa sassan da bututun man fetur ke shinfide a karkashin kasa.

Kana zuwa yanzu jami’an kashe gobara ta gwamnatin jihar Legas da na tarayya sun yi kokarin kashe wutar, haka zalika jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta kasa wato NEMA a takaice sun isa wajen domin bada agaji.

Babban jami’in hukumar da ke kula da shiyyar jihohin Kudu maso Yamma Ibrahim Farinloye, ya shaida cewa wutar ta tashi ne daga inda bututun man fetur din suke, ya ce an girke manyan motocin kashe gobara 3 da suke aikin kashe wutar kana zuwa yanzu ba za a iya sanin adadin mutanen da suka hallaka sakamakon gobarar ba, sai dai gidaje akalla 50 sun salwanta a sakamakon ibtila’in.

Wasu daga cikin gidajen da gobarar ta lakume