Gobara ta ci wasu shaguna biyu a kasuwar Kurmi da ke birnin Kano a ranar Talatar da ta gabata.
Kamar yadda wasu rahotanni daga birnin suka bayyana, gobara ta tashi
ne da misalin karfe takwas na daren ranar Talatar da ta gabata.
Wani ganau wanda yake da shago a kasuwar, Auwalu Skido Mai riguna, ya shaida wa BBC cewa shaguna biyu ne na kayan doki suka kone.
Mutumin ya ce bayan da suka ga wutar na ci a shagunan saboda gudun kada ta kama sauran shaguna, sai suka kira jami’an kashe gobara, kuma ba da jimawa ba suka zo suka kashe wutar.
Ya kuma kara da cewa akalla kayan da suka kone a shagunan sun kai na naira miliyan uku. Ba a dai samu asarar rai ko daya a gobarar ba. Wannan dai ba shi ne karon farko da gobara ta tashi a kasuwar ba, don a baya an sha samun faruwar hakan.
Gobara ta ci shaguna a kasuwar Kurmi
Gobara ta ci wasu shaguna biyu a kasuwar Kurmi da ke birnin Kano a ranar Talatar da ta gabata.Kamar yadda wasu rahotanni daga birnin suka…