✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ghana ta lashe amanta kan gargadin barazanar ta’addancin a Abuja

Sanarwa ta ce, ’yan Ghana na zaune lafiya da ’yan uwansu ’yan Najeriya, kuma babu wata barazana ga rayuwarsu ko kuma dukiyoyinsu.

Ghana yi amai ta lashe kan gargadin da ta yi wa ’yan kasarta na zuwa Abuja a bisa fargabar barazanar ta’addanci.

Gwamnatin Ghana ta janye sanarwata tare da bayar da hakuri ga Najeriya ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis.

Ma’aikatar Harkokin Kasashen Waje ta kasar ta kuma ce, ba ta da masaniyar wata barazana ga ’yan kasar mazauna Najeriya sannan ta nemi afuwa dangane da gargardin, wanda ta ce ba ta ma san da shi ba, duk da cewa da sunanta a ka yi.

Sanarwa ta ce, ’yan Ghana na zaune lafiya da ’yan uwansu ’yan Najeriya, kuma babu wata barazana ga rayuwarsu ko kuma dukiyoyinsu.

A ranar 16 ga watan Nuwamba ne ma’aikatar ta fitar da wata sanarwa da ke gargadin ’yan kasar Ghana da su guji zuwa Abuja, sai idan zuwa birnin ya zama dole.

Sanarwar ta lissafa ta’addanci, da garkuwa da mutane, da sauran matsaloli na tsaro a matsayin hujjar ta yin gargadi.

 

Vanguard.