✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fatima Zahra Umar: Tsaro hujja daga kotu zuwa kafofin sadarwa

Fatima Zahra Umar sananniya ce wajen gwagwarmayar ganin mata sun samu ta-cewa

Barista Fatima Zahra Umar lauya ce, amma daga bisani ta tsunduma harkar yada labarai, musamman a bangaren wayar da kan mata.

Da farko dai ta kirkiro wani shafin intanet (blog) mai suna Divorce Diaries wanda yake duba a kan yadda aurarraki ke durkushewa.

Da yake an ce ga na gaba akan ga zurfin ruwa, shafin na yin nazari a kan wannan lamari ne da nufin gano ummulhaba’isun mutuwar auren ko wasu sa dauki darasi.

Bayan nan, ta hada gwiwa wajen kirkiro mujallar intanet ta “Jaruma” ta kuma zama Babbar Editar mujallar.

Muryar matasa

Wannan mujalla ta taka muhimmiyar rawa wajen fitowa fili da batutuwan da ke da muhimmanci ga mata, da ba su shawarwari a kan yadda za su bayar da gudunmawa wajen ciyar da al’umma gaba.

Tauraruwar tamu ta kuma gabatar da Shirin “Adikon Zamani” a Sashen Hausa na BBC, inda take tattauna wasu batutuwa da suka shafi mata wadanda ba kasafai ake magana a kansu ba.

Ta hanyar sirin, Fatima Zahra Umar ta taimaka wajen wayar da kan mata game da wasu muhimman abubuwan da ba su fahimce su ba, amma wasu dalilai suka hana su neman karin bayani.

Sannan kuma ta yi fice a fagen fafutukar ganin ana damawa da mata da matasa a harkokin siyasa.

Mai yiwuwa ma matukar sha’awar da take da ita ta ganin matasa sun shiga an yi da su ne ya sa take da burin zaman Gwamna watan wata rana.

Abar koyi a Arewa

A shekarun 2016 da 2017, Fatima Zahra Umar ta shiga cikin jerin matasa 100 masu karfin fada a ji a Arewa.

A shekarar 2018 kuma ta shiga cikin mata matasa kalilan da aka saka a cikin Kwamitin Shirya Babban Taron jam’iyyar APC na Kasa da Kwamitin Shirya Zaben Fitar da Dan Takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar.

A yanzu haka, Tauraruwar tamu tana aiki ne a Ofishin Shugaban Majalisar Dattawa a matsayin mataimakiya ta musamman a kan al’amuran da suka shafi mata.