Fadar Shugaban Kasa ta ce kasar tana fuskantar karancin kudi da fasahar zamani don kai agajin gaggawa ga dimbin mutanen da bala’o’i suka aukawa a kasar.
Fadar ta bayyana cewaduk da haka gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari za ta yi bakin kokarinta ta kai agajin gaggawa ga wadanda bala’i ya aukawa a kasar.
Babban Mai Taimakwa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labari da Wayar da Kan jama’a, Malam Garba Shehu shi ne ya bayyana haka a shirin Hannu da Yawa na gidan Rediyon Kaduna wanda aka gabatar a karshen mako.