✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dundumin dundumdurundum

Cin-duhu da cincirindon camamar cacumar Hauro da ’yan wantanda suka tsuwurwurta a tsawon shekarun mulkin mulaka’u na Jam’iyya mai dan boto da sanda jirge shi…

Cin-duhu da cincirindon camamar cacumar Hauro da ’yan wantanda suka tsuwurwurta a tsawon shekarun mulkin mulaka’u na Jam’iyya mai dan boto da sanda jirge shi ya haifar wa Haurobiyawa dundumi, inda na-mujiyar al’umma ya kanne daga hango kulle-kulle, ballantan su iya warware kowace irin tufkar makirci. Ni dai ba kamfanin dundum durundum ni ke bayani a kai ba, domin tuni an dade da cefanar da wannan mabubbugar haskaka Haurobiya, inda aka karke da zama Jamhuriyar ja-ni-ina-reto. Wannan jamhuriya ta haifar da gobara da turnukewar hayakin da ya haifar mana da dundumi.
Haurobiyawa, daukacin gama-garin al’umma sun taka tudun laifuffukan da hannayen su ke tsuwurwurtawa, don haka dundumi ya baibaye mu, har mun kasa fasko illar miyagun ayyukan mu muna hango na wasu. daukacin jaridu da mujalllun kasar Haurobiya, har ma da akwatunan maganganu da masu hotuna, duk dibge suke da batutuwan ’yan watanda, musamman masu kwashi kwaraf da dukiyar al’umma. Kai na tabbata da yawa daga cikin Haurobiyawa sun gaji da jin labarin su Santal kwaiduwa da In-gwangwaje-in-wala da Fuffuken-fakan-fayau da Ina-ina-ta’adi da Samun-bom-da-sauki da makamantan su.
Kai tun daga kan Gwamnatin Baba-ojo mai gonakin Ottawa zuwa Gudun-loko da Jona-tantin mulki duk an yi cuwa-cuwar cin ca’ammas tamkar ana birnin Tagadas, hart a kai ga an karairaya Hauro baras, ta fadi kasa warwas. Kai hatta Gwamna gwarangwam na Jihar Bararon-nono wasu na gani ya handame makudan matsabbban kananan hukumomin da masu haramta bobo da kwambon boko suka tarwatsa al’ummar su. Gwamnonin da suka karbi ’yan matsabban “Belin-auta,” suka karke da “Billen-wauta sun yi tarayya wajen tafka ta’asa a kwanon tasa, har ma da barambarama da barusa.
’Yan makaranta masu koyon watsatttsake da buda wagagen littattafai a farfajiyar Dodorido da ke cikin Amintacciyar jaridar kasar Haurobiya, ya kamata ku fasko cewa, a shekara ta dubu karamin lauje da kwanciyar magirbi da Haurobiyawa da daukacin mutasnen Ifrikiyya suka dura wa Dokta James Watson, mai watso-watso, wanda ya yi watsa-watsa da basirar bakin mutum ashariya, sai muka yi likimo, inda muka nusar da ku cewa, “ba a fasko manufarsa ba.” Masu bibiyar wannan makaranta idan har ba su kakaba wa kurungun su tagiyar Malam Mantau ba, sun san, na bijiro wa ‘Bakin mutum na da dimbin basirar da ta zarce ta kowace al’umma a fadin duniya, musamman mu Haurobiya da muka kware wajen kwarar junanmu. Domin masu kaifin basira a cikin gungun talakawa da sun yi hakoron warware sasarin talalar talauci, nan take za su ci wa kowa mutunci; tunda mu ke da masu ayyukan tsayuwa bisa kafa guda da sili da manuniyar sama; ga ’yan yawon damun-fura a wajen yawon-dara.
Bisa la’akari da kwarewar kwararru wajen kwarar al’umma, na fasko cewa, akwai bukatar Gwamnatin Haurobiya ta tsara yadda ’yan kwadago masu lalube kadago, ko lada da la’adar curin mandako a dan koko, a rika biyan su albu\kata, amma ba abin biyan bashi ba; su kuwa ’yan fansho a daina yi musu fanco; ’yan makaranta na bukatar manhaja mara hajijiya, ta yadda za a daina juwa-juwa wajen juya akalar al’umma.
Kwananan nan na bijiro da yadda za a tallafi rayuwar matasa masu fuka0fukin tashi, mutanen Mista Darlung da ke gararamba a Kangon Mista Gizagong, inda n ace, wadanda ke Jihar Filfilon-toto lallai a ba su tallafin Gwmana Lalong, su kuma su kafa Kantin Dong Fong irin na mutanen Mao Zedong.
kin bin shawarwarin wannan katafariyar makaranta ta sanya kuke ganin dimbin matasa na ta zabarin cabi a kan baburido, har wasu kan sawo Jincheng, su je nan, su je cang; wasu kuwa su dare bisa Zongcheng, su je wurin ’yan matang don yin zanceng. In ban da batanbaka-tantan, ai darewa bisa tsuntsun soyewar zukata ba zai taba burge dakwalwar budurwa ba, matukar babu ’yan matsabban sayen hatsin dundume kururu.’
Lallai dalili ya yi da Jam’in jam’ar jami’ar Gamji gijigin masu bobo da kwanbon boko da ke birnin Lawurje za ta shirya mana manhajar fardar garka da gayauna; ko jami’an jami’ar shehu mujadaddi da ke birnin Shehu ta nusar da mu yadda za mu daina dogara kacokam wajen neman kWADAGON FARAR KWALA. Batu na ingarman kwangiri kwadagon farar kwala ya haifar mana da dimbin masu kwalema a lalitar kasar Haurobiya. Direbobin alli da jami’an Asusun ilimi a hanzarta wajen lalubo maganin dundumi da ya kange mana na-mujiya, ha rake ta yi mana cin duhu a cikin dundumdurundum.

Sakon makaranta:

Cigiyar dalibai
Assalamu alaikum.
Ina yi wa dukkanin Tsofaffi da Sababbin dalibai fatan alkhairi, Allah kuma ya kara wa Haurobiya zaman lumanar uwarjiki. Na kasance cikin alhinin yadda darusan makaranta suke nema su tabarbare, sam nema muke yi mu zama kyanwar Innarmu, mai sunan miya ba gishiri da tsokar nama.
dalibai sun bar Babban Dodo da aiki, idan ba domin jarumi yake ba, da yanzu makaranta ta kasance kamar ta yaran GizBaba. ’Yan bayan kango masu barci da na-mujiya sili.
Ina mutumin Kudan me sunan Baba na  Jihar bayan kada?
Ina Sameer Bala?
Ina Alu -Jaa Bin Madda? Ya kamata ku  dawo a dora daga inda aka tsaya. Ina amfani da wannan dama wurin yi wa Shugaban dalibai ta’aziyyar rashin mahaifinsa, Allah ya gafarta masa.
Ashiru dan-Azumi Gwarzo [email protected] ,07036589807