✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dole mu hadu mu yaki talaucin da yake a Najeriya – Tinubu ga Gwamnoni

Ya ce a shirye yake ya yi aiki da su wajen dakile talauci a kasar

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya yi kira ga Gwamnoni da su hada kai da Gwamnatin Tarayya wajen yaki da talauci a Najeriya.

Shugaban, wanda ya yi wannan kiran lokacin da ya karbi Gwamnonin Najeriya a fadarsa da ke Abuja ranar Laraba, ya ce yawan talaucin ba abin da za a lamunta ba ne.

Tinubu ya kuma yi kira ga ’yan siyasa da su manta da bambance-bambancensu su hada gwiwa wajen kakkabe talauci a Najeriya.

Ya ce, “Muna ganin tasirin talauci a fuskokin mutane da yadda talauci ya zame musu kamar gado. Babban abin da muka sa a gaba shi ne yaki da talauci ta hanyar ajiye bambance-bambancenmu da gina kasa,” kamar yadda sanarwar Daraktan Yada Labarai na Aso Rock, Abiodun Oladunjoye ya fitar.

Ya kuma ce, “Dukkanmu ’yan gida daya ne da muke barci a dakuna daban-daban. Idan muka kalli junanmu a haka muka yi aiki tare, za mu cire mutanenmu daga talauci.”

Shugaba Tinubu ya kuma ce shugabanci na gari ne zai tabbatar da ci gaban Dimokuradiyya a Najeriya.

Kazalika, ya kuma ba Gwamnonin tabbacin cewa kofarsa za ta zama a bude ga dukkan Gwamnonin.