✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa

Ƙungiyar ta ce rikicin da ke faruwa a Ribas bai kai matakin da za a ayyana dokar ta-ɓaci ba.

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF), ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu da gaggauta janye dakatarwar da ya yi wa Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin jihar.

Da yake magana a madadin ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya ce babu wani dalili da ya dace da zai sa shugaban ƙasa ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar.

Ya bayyana cewa, kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanadi ayyana dokar ta-ɓaci ne kawai a lokuta na matsanancin rikici kamar yaƙin basasa, ko rushewar doka da oda, wanda a cewarsa babu ɗaya daga cikinsu da ya faru a Jihar Ribas.

NEF, ta zargi Gwamnatin Tarayya da yin hakan ne saboda son rai, ba don amfanin al’umma ba.

Ƙungiyar ta yi zargin cewa rikicin siyasar yana da nasaba da taƙaddamar da ke tsakanin gwamnan da aka dakatar da tsohon gwamnan jihar wanda yanzu ministan Gwamnatin Tarayya ne.

Dattawan sun buƙaci gwamnati da ta dawo da dimokuraɗiyya, adalci, da zaman lafiya a Jihar Ribas.

Haka kuma, sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da kada ta bari irin wannan rikicin siyasa ya tsananta a wasu jihohi kamar Kano, inda ake ci gaba da samun saɓani dangane da masarautar Kano.