✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Damben gargajiya ya fara kankama a Jihar Ogun

Mutane maza da mata masu sha’awar kallon wasan damben gargajiya a Jihar Ogun suna tururuwa zuwa garin Ogere, dake kan babbar hanyar Edpress ta Ibadan…

Mutane maza da mata masu sha’awar kallon wasan damben gargajiya a Jihar Ogun suna tururuwa zuwa garin Ogere, dake kan babbar hanyar Edpress ta Ibadan zuwa Legas domin kashe kwarkwatar idanu. Wakilinmu yana daga cikin dimbin mutane da suka yanki tikiti a gidan wasan dambe na Ogere domin kallon wasan damben gargajiya na yammacin ranar Lahadi da aka gwabza a tsakanin zaratan ‘yan dambe da suka yi fice a wannan sashe musamman bangaren Kudu da Arewa.
 Wakilinmu ya ce, Shagon Duragon daga Arewa da Shagon Sikido daga Kudu su ne suka fara karawa a wasan farko a inda suka yi ta naushin juna a turmi na daya ba tare da kisa ba, amma a lokacin da aka dawo turmi na biyu bayan ‘yan mintuna kadan sai Shagon Sikido ya kai wa Shagon Duragon naushi a fuskarsa wanda a nan take ya gigice ya zube a kasa har da hade da koriyar majina da ta rika fita a hancinsa.
 Har ila yau an yi wata gwabzawa a tsakanin Garkuwan Kaduna daga Kudu da Shagon dan Garba daga Arewa wanda aka dauki tsawon lokaci kowanensu yana nuna irin kwarewa da bajintarsa har zuwa turmi na uku da Shagon dan Garba ya kai naushi ga Garkuwan Kaduna wanda ya yi kokarin kaucewa amma sai hannun hagunsa ya tabo kasa kuma aka tabbatar da an kashe shi. A wannan lokaci magoya bayan Garkuwan Kaduna daga Kudu sun yi kokarin nuna rashin amincewa da wannan kisa domin a cewarsu, santsin ruwa ne ya sa hannun Garkuwa ya taba kasa a lokacin da yake kaucewa naushin amma ba naushi ne ya kashe shi ba. An dai tabbatar da wannan kisa bayan gajeruwar jayayya a tsakanin bangarorin Arewa da Kudu. Kuma mawaka da makada sun yi ta zagayawa da wadanda suka yi nasara suna samun kyautar kudi daga ’yan kallo. Kisa biyu kawai aka yi a dukkan fafatawar da aka yi a wannan rana.
 Mataimakin Shugaban Gidan Damben gargajiya na garin Ogere, a Jihar Ogun, Malam Lawalli Musa Argungu, da ake yi wa lakabi da dan Maliki ya ce duk da yake wasan damben gargajiya ya samu gindin zama a garin Ogere, “sai dai har yanzu bamu fara cin ribar dambe ba domin da kudin aljihunmu muke dauko mawaki da gayyatar wasu ‘yan dambe daga wasu wurare na kasa.”
 Da yake yi wa wakilinmu takaitaccen bayani na tarihin fara wasan dambe a garin Ogere, dan Malki ya ce, “ yau shekaru 5 da wucewa kenan da wani mutum mai suna Nasiru, ya fara bude gidan dambe a garin Ogere. Bayan rasuwarsa ne sai abin ya tsaya daga baya ne Sarkin Yaki Goje, tare da goyon bayan mutane 10 har da ni mataimakinsa muka hada kudi muka gayyato mawaki da tawagarsa daga Legas  don farfado da wannan wasa. Mun kulla yarjejeniyar  daukar dawainiyar kudaden albashinsu da sauran bukatun su baki daya kuma, Goje ya samu nasara ne saboda tsoron da dukkan ‘yan gareji suke yi masa domin babu wanda ya isa ya lakuci hancinsa. Su kuma ‘yan dambe akwai wadanda muke gayyata akwai kuma masu kawo kansu. Kafin mu kai ga nasarar kafa gidan dambe sai da muka yi dauki ba dadi da wasu mutane da suka nemi tayar da zaune tsaye a tsakaninmu dasu. Wannan ne yasa shagaban gidan dambe Goje, ya dauki matakin fatattakarsu daga wannan gari baki daya.”
 “Wallahi muna yin wannan abu ne domin ci gaban wannan gari amma ba domin riba ba. Idan domin riba ne, ni dai da tuni na yi gaba amma saboda sha’awar dambe da kara farfado da al’adunmu na gargajiya da bukatar ci gaban garin Ogere, shi ne yasa muke kashe dimbin kudin da babu riba domin tabbatar da ganin wasan ya zauna da gindinsa. Yanzu gashi ita kanta gwamnatin Jihar Ogun ta sanya garin Ogere a cikin jerin sunayen garuruwa da ta san da zamansu kuma duniya ma ta san da wannan gari wanda wannan wasa na damben gargajiya shi ne yake kara janyo hankalin jama’a da suke zuwa domin kallon wasa da muke yi da safe karfe 10 da kuma yammacin kowace rana da karfe 4 da rabi.”
 Shi kuwa Sakataren gidan dambe na Ogere, Malam Aminu S. Fawa cewa ya yi, “ba mu kai ga fara tuntubar ma’aikatar wasanni ta jihar Ogun domin sanya wasan dambe a jerin wasanni a jihar ba tukuna, muna so ne idan komai ya kankama daga bangarenmu sannan ne za mu isar da kanmu gare su. Muna mika rokonmu ga gwamnati, da zarar mun mika kanmu gare ta to, ta tabbatar da cewa, ta amshe mu da hannu biyu ta yadda za mu ci gaba da gudanar da wannan wasa ba tare da takurawa ba kuma zai iya samar da kudaden shiga ga gwamnati.”.