✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

COVID-19: Karin mutum biyar sun kamu a Jigawa

An samu karin mutum biyar da suka kamu da cutar coronavirus a kananan hukumomin Dutse da Auyo da Miga da Gwaram a jihar Jigawa. Kwamashinan…

An samu karin mutum biyar da suka kamu da cutar coronavirus a kananan hukumomin Dutse da Auyo da Miga da Gwaram a jihar Jigawa.

Kwamashinan lafiya na jihar Dokta Abba Zakari Umar, ne ya tabbatar da hakan, yana cewa mutum biyu aka gano suna dauke da cutar ne a Dutse, mutum daya a Miga da mutum daya a Gwaram sai kuma mutum daya a garin Auyo.

“Yanzu haka a jihar Jigawa akwai mutum tara da suka kamu da cutar, amma mutum daya daga cikinsu ya rasu a karamar hukumar Dutse.” Inji Kwamishinan.

Kwamashinan, ya kara da cewa an dauki matakin rufe kananan hukumomin da abin ya shafa daga karfe 12 na daren ranar Juma’a mai zuwa.

Ya kuma ce, an umarci al’ummomin kananan hukumomin su tanadi kayan abinci don ganin ba a samu wata matsala ba.

Dokta Umar, ya kara da cewa tuni gwamnatin jihar ta dauki matakin raba kayan abinci da kudi ga wadanda aka hana fita domin a ragewa al’umma radadin da za su iya fadawa ciki.

Ko a ranar Talata ma dai gwamnatin ta Jigawa ta kafa dokar hana fita a garuruwa uku na jihar bayan da aka samu wasu mutane sun kamu da cutar.